Yanayin siyasa a Nijar bayan zaɓen shugaban ƙasa
March 15, 2011Jamhuriya Nijar ta shiga wani saban baben siyasa, bayan zaɓen shugaban ƙasa zagaye na biyu.
Saban shugaban Alhaji Mahamadou Issoufou ya gana da shugabanin ƙawancen jam´iyun da su ka taimaka masa ya lashe zaɓe.
A ɗaya wajen masharahanta a game da harakokin siyasa sun fara tsokaci game da makomar siyasar Nijar.
Za ku saurari rahotanin ɗaya na bin ɗaya har guda ukku.
Na farko game da makomar mulkin ƙawance a Nijar, sai kuma rahoto daga wakilinmu na birnin Yamai Mahaman Kanta game da ganawar da aka yi tsakanin Mahamadou Issoufou da abokan ƙawancensa, sannan rahoto na ukku, inda wakilinmu Gazali Abdu ya yi hira da Dr Ado Mahaman, wanda ya yi nazari dangane da darrusan da za a iya ɗauka a zaɓen da ya wuce.
Sannan rahoto an ukku, shima nazari game da batun ƙawance tsakanin jam´iyun siyasar Nijar.
Mawallafi: Yahouza Sadissou Madobi
Eidta. Usman Shehu Usman