SiyasaGabas ta Tsakiya
Yan jaridar Falasdinu 184 aka kashe a Gaza
August 12, 2025Talla
Wasu daga cikin 'yan jaridar na Falasdinu an kashe su a lokacin da suke tsaka da gudanar da aiki a fagen daga ko kuma a cikin gidaje da iyalansu, wasu kuma a lokacin da suke rangadin neman rahoto duk da cewa suna dauke da tambarin aikin jarida na "PRESS" ko kuma a asibitoci da sansanonin 'yan gudun hijira da wajen karbar abinci da ke kasancewa tudun muntsira.
Karin bayani:'Yancin aikin jarida ya samu nakasu a duniya
Ana samun mabambantan alkaluma da kuma kididddiga kan adadin manema labaran da ake kashe wa a yakin Isra'ila da mayakan Hamas. Kwamitin CPJ ya sanar da cewa yayi amfani da binciken kwakkwafi wajen tattara alkaluman 'yan jaridar da aka halaka a Gaza.