Harin 'yan bindiga ya hallaka gomman mutane a jihar Taraba
May 25, 2025Gwamnan jihar Agbu Kefas a wata sanarwa da ya fitar ya ce mutane da dama sun rasa rayukansu da dukiyoyinsu a wannan harin na ranar Asabar, duk da cewar gwamna Kefas bai bayyana adadain wadanda suka rasa rayukansu a wannan mumunan harin ta'addancin ba.
Sai dai shaidun gani da ido sun tabbatar wa kamfanin dillancin labarai na AFP sun ga gawawaki 16 warwatse a kauyen Munga da ma wanda ya tabbatar da ganin 13 a kauyen Magani.
A baya-bayan nan wannan yanki na jihar Taraba na fama da barazanar hare-.haren 'yan bindiga wadanda suke kashe mutane dama yin awon gaba da wusu.
Wannan shi ne hari mafi muni da jihar Taraba ta gani tun bayan dawo wa da hare-haren 'yan bindiga. Matsalar tsaro musamman a arewacin Najeriya na ci gaba da addabar al'umma duk da kokarin da sojojin kasar ke cewa suna yi.
Karin Bayani: Sabon yanayi na tabarbarewar tsaro a Najeriya