You need to enable JavaScript to run this app.
Tsallake zuwa shafin jadawali
Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Bidiyo
Shirye-shiryen DW Hausa
Yankuna
Najeriya
Nijar
Afirka ta Yamma
Sassa
Siyasa
Zamantakewa
Wasanni
Mayar da hankali
Ilimin Fasahar Zamani
Shirye-shiryen DW Hausa
Bidiyo
Talabijin kai tsaye
Talla
Turai
Turai nahiya ce daga cikin nahiyoyin da muke da su a duniya.
Tsallake zuwa bangare na gaba Duk abin da ya shafi wannan maudu'i
Duk abin da ya shafi wannan maudu'i
Kungiyar Taraiyar Turai ta janye batunta na kaiwa kasar Iran Majalisar Dinkin Duniya
Kasashen Burtaniya,Faransa da Jamus,sun dakatar da batunsu na kaiwa kasar Iran gaban komitin sulhu,yayinda kasar Rasha take nuna adawa akan wannan batu.
Takaddama tsakanin tarayyar Turai da China dangane da tufafin kasar
Wata tawagar kwararrun tarayyar Turai zata je China don tattaunawa da nufi gano bakin zaren warware wannan takaddama
Dangantakar Iran da kungiyar hadin kan Turai
Kasar Iran da kungiyar hadin kan Turai sun kasa shawo kan sabanin dake tsakanin su game da tashar nuclear
An yi karar kungiyar tarayyar Turai dangane da dokar kayyade shigo da tufafi daga China
Kamfanin Gelco da ke birnin Geilenkirchen ya yi fatan cewa wannan karar zata janyo hankalin jama´a.
Kasuwancin sukari a Kungiyyar hadin kan Turai
Masu harkar kasuwancin sukari a nahiyar Turai, sun fara nuna damuwarsu ga garambawul din da ministocin noma na Kungiyar Hadin Kan Turai ke niyyar yi wa tsarin kasuwancin sukarin, sakamakon angaza wa Kungiyar EU da Kungiyar ciniki ta duniya wato WTO ke yi.
Taron majalisar Turai
A yau sakataren harkokin wajen Birtaniya Jack Straw ya gabatar da jawabi ga majalisar Turai akan matakin taimakon Afurka
Shugaba Schröder ya yi kira ga ba da kaimi wajen shawo kan matsalolin da Kungiyar Hadin Kan Turai ke huskanta a halin yanzu.
A halin yanzu, Kungiyar Hadin Kan Turai ta sami kanta ne cikin wani mawuyacin hali, bayan zabukan raba gardamar da aka gudanar a kasashen Faransa da Netherlands, inda `yan „na ki “, suka fi samun rinjayi. Firamiyan kasar Luxembourg, Jean-Claude Juncker, wanda kasarsa ce ke jagorancin kungiyar a halin yanzu, yana nan yana ta kokarin ganawa da sauran shugabannin kasashen kungiyar, don samad da tsari na bai daya, na irin kamun ludayin da za su yi nan gaba.
`Yan kasar Holland sun yi watsi da kundin tsarin mulkin Kungiyar Hadin Kan Turai.
Al'umman kasar Holland sun bi sahun na Faransa, wajen yin watsi da kundin tsarin mulkin Kungiyar EU. A zaben raba gardamar da aka gudanar a kasar a ran 1 ga watan Yuni, kashi 61% ne suka jefa kuri'un kin amincewa da kundin.
Al'umman Faransa sun ce "non", ga kundin tsarin mulkin Kungiyar Hadin Kan Turai.
Sakamakon zaben raba gardamar da aka gudanar a ran 29 ga watan Mayu na nuna cewa, masu adawa da kundin tsarin mulkin Kungiyar Hadin Kan Turai ne suka ci nasara. Ko wane irin hali Kungiyar za ta sami kanta a ciki a halin yanzu ?
Ziyarar Bishop-Bishop na Afurka da Asiya da latin Amurka a Turai
Bishop-Bishop na mujami'ar Katolika daga kasashen Afurka da Asiya da Latin Amurka na ziyarar kasashen Turai domin ba da kwarin guiwar daukar karin matakai a yaki da matsaloli na talauci da yunwa a duniya
Matsalar wariya a Turai
Rashin cikakkun bayanai a game da matsalar wariya na hana ruwa gudu a kokarin dakatar da hare-haren masu zazzafan ra'ayin wariya a nahiyar
Ziyarar Shugaba Bush Ga Nahiyar Turai
A yau litinin ne shugaban kasar Amurka George W. Bush ya fara wata ziyara ta yini biyar ga kasashen Turai
Sabuwar dangantakar Amurka da kawayenta a nahiyar Turai
A ziyarar da take ga kasashen Turai sabuwar sakatariyar harkokin wajen Amurka Condoleeza Rice ta yi kiran bude wani sabon babi ga dangantakar Turai da Amurka
Barroso ya gabatar da manufofinsa ga majalisar Turai a birnin Brussels
Sabon shugaban hukumar zartaswar kungiyar EU Jose Manuel Barroso ya gabatar da jerin ayyukan da hukumarsa ta kuduri aniyar yi a cikin shekaru 5 masu zuwa.
Kungiyar Tarayyar Turai (KTT) Zata Fara Shawarwarin Karbar Turkiyya
A taron kolinsu da suke gudanarwa a Brussels shuagabannin kasashen KTT sun amince da gabatar da shawarwarin karbar Turkiyya a kungiyar daga uku ga watan oktoban shekara ta 2005
ZARTAR DA MAJALISAR TURAI.
Cinikin Makaman KUngiyar Tarayyar Turai
Kasashen KTT, musamman Birtaniya da Faransa da Jamus da Italiya da Sweden, suna daga cikin gaggan kasashen da suka fi cinikin makamai a duniya
Daftarin Tsarin Mulkin Turai
A gobe juma'a idan Allah Ya kai mu za a yi bikin rattaba hannu kan daftarin tsarin mulkin Turai a birnin Rom
Sabon Kudurin Ciniki Tsakanin Kasashen Turai Da Kasashe Masu Tasowa
Kungiyar Tarayyar Turai zata sauya salon cinikayyarta da kasashe masu tasowa tun daga shekara ta 2006
Yawancin kasashen Turai sun nuna gamsuwa da shigar turkiyya cikin Kungiyar EU
A ranar laraba kungiyar gamaiyar Turai zaa tantance ko kasar Turkiyya zata iya shiga cikin tattaunawar shiga cikin kungiyar a nan gaba
Matsalolin 'Yan Afurka A nahiyar Turai
A cikin wata hikayar da ta rubuta Fatou Diome daga kasar Senegal tayi bayani filla-filla a game da matsalolin da 'yan Afurka ke fama da shi a nahiyar Turai da kuma barazanar da suke fuskanta akan hanyarsu ta shigowa nahiyar
Shawarwarin Karbar Turkiyya A Kungiyar Tarayyar Turai
Bisa ga ra'ayin kantoman KTT akan karbar karin kasashe Günter Verheugen kasar Turkiyya ta samu ci gaba matuka ainun ta yadda za a iya tsayar da wani takamaiman wa'adi na fara shawarwari da ita
Rikici Game Da Hukuncin Kotun Turai
Kafofin yada labaran Jamus sun bayyana bacin ransu a game da hukuncin kotun Turai dake birnin Strassburg dangane da abin da suke ganin tamkar wani yunkuri ne na kayyade 'yancin 'yan jarida a nahiyar Turai
Makomar kungiyar tarayyar Turai EU.
DUBBAN BAKIN HAURE NA KWARARA ZUWA TURAI TA SPAIN DA MOROKKO DAGA AFRIKA.
Ana cigaba da fuskantar matsalar kwararan bakin haure zuwa kasashen turai,musamman daga yankunan Sahara da Afrika.
Rage yawan sojojin Amirka a nahiyar Turai
Kungiyar EU da Majalisar shawara ta kasashen Turai
RIKICIN WARWARE MATSALAR KAURA A JAMUS DA NAHIYAR TURAI.
Har ila yau dai, ana ta ci gaba da muhawara kan shawarar nan da ministan harkokin cikin gidan Jamus, Otto Schilly ya gabatar, na fara jibge makaurata zuwa Turai, a arewacin Afirka, kafin a ji koke-koken da suke tafe da shi. Akwai dai masharhanta da dama da suke adawa da wannan ra'ayin.
AN ZABI JOSÉ MANUEL BARROSO TAMKAR SABON SHUGABAN HUKUMAR TARAYYAR TURAI
Majalisar tarayyar Turai, ta zabi tsohon Firamiyan kasar Portugal, José Manuel Barroso tamkar shugaban Hukumar kungiyar EU. Zai dai fara aiki a wannan mukamin ne a ran 1 ga watan Nuwamba. Kafin wannan lokacin kuwa, yana da gagagrumin aiki a gabansa, wato na zaban rukunin kwamishinoni 24, wadanda tare ne za su dinga tafiyar da harkokin kungiyar.
Shugabancin Kasar Netherlands Ga Kungiyar Tarayyar Turai
A yau laraba ne P/M kasar Netherlands Jan-Peter Balkanende ya gabatar da jawabi a game da manufofinsa ga majalisar Turai dake Strassburg
Matsalar Manema Mafakar Siyasa A Nahiyar Turai
Ministan cikin gida na Jamus Otto schily ya fuskanci kakkausan suka daga kungiyoyin kare hakkin manema mafakar siyasa dangane da shawararsa game da bude kafofin bitar takardun manema mafakar siyasar a kasashen arewacin Afurka domin hana makaurata tuttudowa zuwa nahiyar Turai
Majalisar Turai Ta Nada Shugabanta
A zaman farko da tayi bayan zaben da aka gudanar watan yunin da ya wuce a yau talata majalisar Turai ta nada Josep Borrell domin shugabancinta na tsawon shekaru biyu da rabi
Matsalar Manema Mafakar Siyasa A Nahiyar Turai
An sake shiga wata sabuwar mahawara a game da karbar 'yan gudun hijira a kasashen Kungiyar Tarayyar Turai sakamakon tabargazar nan ta Cap Anamur a tekun Bahar Rum
Sanarwar Gwamnati Akan Daftarin Tsarin Mulkin Kasashen Turai
A zaman mahawarar da suka gudanar a yau juma'a dukkan wakilan majalisar dokokin Jamus ta Bundestag sun yi marhabin da daftarin tsarin mulki bai daya na kasashen Turai
Sakamakon Taron Kolin Shuagabannin Kasashen Kungiyar Tarayyar Turai
A taronsu na yini biyu shuagabannin kasashen KTT sun cimma daidaituwa akan daftarin tsarin mulki bai daya tsakaninsu
Zaben Majalisar Turai
A jiya lahadi ne aka gudanar da zaben majalisar Turai, to sai dai kuma yawan wadanda suka shiga zaben bai taka kara ya karya ba
Zaben Majalisar Turai A Ranar Lahadi Mai Zuwa
A ranar lahadi mai zuwa ne za a gudanar da zaben majalisar Turai mai wakilai 732, wacce kuma take taka muhimmiyar rawa a zartaswar Kungiyar Tarayyar Turai
Rahoton Hukumar Majalisar Turai Akan hakkin Dan Adam
A cikin rahoton da ta bayar dangane da Jamus Hukumar Majalisar Turai akan hakkin dan-Adam, ko da yake ta ya ba da irin ci gaban da aka samu a kasar amma tayi gargadi a game da barazanar kyamar baki dake da yada yaduwa, musamman a gabacin kasar
Dangantakar Turai da Afurka
Kasashen Turai kan mayar da hankali ga al'amuran Afurka ne a daidai lokacin da nahiyar ke fama da kaka-nika-yi
Dangantakar Kungiyar Tarayyar Turai da Kasar Bailorushiya
Shugaba Lukashenko na Bailorushiya ya ce kasarsa ba kungiya ce ta taimakon jinkai ba kuma a saboda haka wajibi ne ta samu hadin kan kudi daga kasashen Turai domin yaki da bakin haure
Dangantakar Kasashen Kungiyar Tarayyar Turai Da Kasashe Masu Tasowa
Bisa ga dukkan alamu a yanzun za a shiga wani sabon yanayi a game da dangantakar kasashen Turai da kasashe masu tasowa sakamakon karbar sabbin kasashen da aka yi a KTT
Tuntubar 'yan Takarar Majalisar Turai Ta Kan Internet
Tashar DW ta bude wani shafi na musamman domin ba wa jama'a wata kafa ta tuntubar 'yan takarar majalisar Turai na illahirin jam'iyyun siyasar Jamus, kai tsaye
Taron Tattaunawa Akan Matsalar Ta'addanci A Nahiyar Turai
Tashar DW ta dauki nauyin shirya wani taron bita a hadin guiwa da jaridar General-Anzeiger ta birnin Bonn domin tattauna matsalar ta'addanci a Jamus da sauran sassa na nahiyar Turai
Yakin Neman Zaben Majalisar Turai
A ranar 13 ga watan yuni mai kamawa ne za a gudanar da zaben majalisar Turai. To sai dai kuma mutane ba su dauki majalisar da muhimmanci ba, lamarin dake ci wa wakilanta tuwo a kwarya
ZIYARAR MINISTAN HARKOKIN WAJEN IRAN, KAMAL CHARRASI, A JAMUS DA KASASHEN TURAI.
A cikin wannan makon ne, ministan harkokin wajen Iran, Kamal Charrasi, ya fara kai ziyara a wasu kasashen Turai. Ya dai fara ya da zango ne a birnin Brussels, na kasar Belgium, inda kuma nan ne kungiyar Hadin Kan Turai ke da cibiyarta, kafin ya iso a birnin Berlin jiya, inda ya gana da takwarar aikinsa na Jamus, Joschka Fischer da shugaban gwamnatin tarayya Gerhard Schröder. Iran din dai na kokarin inganta huldodinta da kasashen Turai. Amma har ila yau abin da ke hana mata ruwa gudu a wannan yunkurin, shi ne batun nan na makamashin nukiliyan da take mallaka.
Taron Kungiyar Tsaro da Hadin kai a nahiyar turai a Berlin
A yau ne aka bude taron yini biyu na kungiyar tsaro da hadin kai a nahiyar Turai OSCE domin bitar matsalar yaduwar kyamar Yahudawa a kasashen Turai
Shirin karbar sabbin kasashe a Kungiyar Tarayyar Turai
A ranar daya ga watan mayu mai zuwa ne za a kaddamar da bikin karbar sabbin kasashe goma a Kungiyar Tarayyar Turai dake da shekwatarta a birnin Brussels
Taron kolin shugabannin kasashen kungiyar tarayyar Turai a birnin Brussels.
RAHOTANNI SUN TABBATAR DA CEWA YAKIN KASAR IRAQI BA KARAMAR ILLA YAYIWA KASASHEN NAHIYAR TURAI BA;MUSANMAMMA TA HANYAR BARAKA DA AKA SAMU A TSAKANIN SU...IBRAHIM SANI....
KWAMISHINONIN HUKUMAR ZARTARWA NA KUNGIYYAR EU A TSAYE TARE DA SHUGABAN SU A TSAKIYA MR ROMANO PRODI.
An bayyana fadada kungiyar EU zuwa gabashin Turai a matsayin babban matakin farfado da tattalin arzikin nahiyar baki daya.
Shafin da ya wuce
Shafi 39 daga 40
Shafi na gaba