Rikice-rikiceSudan
Ko Khartoum ya zama zakaran gwajin dafi?
August 25, 2025Talla
Wannan dai na nuni da cewa, Khartoum babban birnin kasar Sudan na sake murmurewa daga yakin da kasar ke fama da shi.
Watanni hudu da suka gabata ne sojojin gwamnatin ta Sudan suka sake kwato birnin na Khartoum daga hannun mayakan RSF, yayin da kasar ke ci gaba da fuskantar yanayin yaki.
Tun a watan Afrilun shekara ta 2023 ne, yaki ya barke a kasar tsakanin sojojin gwamnati da Janar Abdel Fattah al-Burhan ke jagoranta da mayakan RSF karkashin Mohamed Hamdan Daglo.